Wani bincike da daliban kiwon lafiya suka gudanar a makarantar firamare ta gwamnati da ke Kwado ya bayyana yadda cunkoso a ajujuwa ke haifar da hadari ga lafiyar dalibai. Daliban, waɗanda ke karatu a Kwalejin Kiwon Lafiya ta Cognate College of Health Sciences, sun gudanar da rangadi a makarantar a ranar 17 ga Fabrairu, 2025, domin wayar da kan ɗalibai kan tsaftar jiki da muhalli (Personal Hygiene).
A yayin rangadin, daliban sun gano cewa a wasu azuzuwa, yawan ɗalibai na haura 370, lamarin da ke iya haddasa yaduwar cututtuka musamman a irin wannan lokaci na zafi. Sun bayyana cewa rashin wadatattun ajujuwa da wuraren wanke hannu na daga cikin matsalolin da ke barazana ga lafiyar ɗaliban makarantar.
Daliban sun gabatar da wasu shawarwari ga mahukuntan makarantar, da suka haɗa da:
Shugaban aikin (Project Coordinator) na makarantar, Malam Faruk Mahuta, ya bayyana cewa matsalolin da aka lissafa ba sabbi ba ne, domin tuni sun sha gabatar da koke ga hukumomin da abin ya shafa, amma har yanzu ba a ɗauki matakin da ya dace ba. Ya yi kira ga Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dr. Dikko Umar Radda, da ya duba halin da makarantar ke ciki domin kawo ɗauki.
A ƙarshe, daliban kiwon lafiya sun raba kyaututtuka kamar sabulu da omo domin tallafa wa daliban wajen tsaftar jiki. Malaman makarantar da daliban da suka halarci taron sun nuna farin cikinsu da yadda aka karɓe su tare da fatan cewa matsalolin makarantar za su samu magani.
Usman Ayuba MASANAWA
Danmasani Radio
Fans
Fans
Fans
Fans