Gwamna Dauda Lawal Ya Rantsar da Hon. Bala Aliyu Gusau a Matsayin Shugaban Hukumar Zaɓe ta Jihar Zamfara (ZASIEC)

top-news


Daga Zaharaddeen Ishaq Abubakar, Katsina Times 

A wani yunkuri na shirye-shiryen gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin Jihar Zamfara, Gwamna Dauda Lawal ya rantsar da Hon. Bala Aliyu Gusau a matsayin Shugaban Hukumar Zaɓen Jihar Zamfara (ZASIEC). An gudanar da bikin rantsarwar ne a ranar Litinin, yayin taron Majalisar Zartaswa ta Jihar, a dakin taro na Gidan Gwamnati, Gusau.

Wata sanarwa daga mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ta bayyana cewa wa’adin shugabancin Sole Administrators na ƙananan hukumomin jihar zai ƙare a ranar 23 ga watan Oktoba, 2024. Saboda haka, wannan rantsarwa na zuwa a daidai lokacin da ake shirin mika mulki ga sabbin shugabannin da za a zaɓa ta hanyar dimokuradiyya.

Sanarwar ta kara da cewa, rantsar da Shugaban Hukumar Zaɓe ta Jihar Zamfara (ZASIEC) an yi shi ne a karkashin jagorancin Babbar Alƙalin Jihar, Mai Shari’a Kulu Aliyu, wadda ta samu wakilcin Mai Shari’a Mukhtar Yusha’u, bisa umarnin Majalisar Zartaswa ta Jihar.

Yayin taron, Gwamna Lawal ya shaida wa 'yan majalisar cewa halartar taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 79 (UNGA) ya yi tasiri matuka ga cigaban jihar. Ya bayyana fatan cewa tattaunawar da aka yi za ta haifar da sauye-sauyen da za su inganta rayuwar al’ummar Zamfara.

Gwamnan ya kuma bayyana cewa ya rattaba hannu kan gyaran dokar zaɓe ta Jihar Zamfara ‘yan makonnin da suka wuce, wanda ya shafi shirye-shiryen zaɓen ƙananan hukumomin da ke tafe. Ya ce: “Bisa hukuncin da Kotun Ƙoli ta zartar kan zaɓen ƙananan hukumomi, wajibi ne mu gudanar da zaɓe a ƙananan hukumomin mu.”

“Bayan rattaba hannu kan gyaran dokar, Hukumar Zaɓe ta Jihar za ta sanar da jadawalin zaɓe cikin gaggawa domin a samu shugabannin da aka zaɓa ta hanyar dimokuradiyya a ƙananan hukumomin jihar Zamfara.”

Gwamna Lawal ya kuma umarci hukumar ZASIEC da ta tsara ka'idoji da tsare-tsare na yadda zaɓen zai gudana, tare da yin kira ga al’umma da su bayar da cikakken hadin kai don nasarar gudanar da zaɓen cikin lumana.

Haka kuma, a yayin taron Majalisar Zartaswa, Gwamna Lawal ya umarci Sakatare na Gwamnati da ya haɗa kai da Mataimakin Gwamna don gudanar da kaddamar da Hukumar Bunkasa Zuba Jari ta Jihar Zamfara (Zamfara State Investment Promotion Agency, ZIPA) da wuri-wuri, domin hukumar ta fara aiki ba tare da jinkiri ba.

A ƙarin bayanin da ya yi, Gwamnan ya sanar da cewa jihar ta kammala shirye-shiryen fara aiwatar da shirin tallafin kuɗi na NG-Cares, wanda zai tallafawa marasa ƙarfi, matasa marasa aikin yi, da mata a faɗin ƙananan hukumomi 14 na jihar. Jimillar kuɗin da za a kashe zai kai Naira biliyan 4.9.

“Za a tallafawa gidaje 5000 masu rauni da buƙatu na musamman, a kuma taimaka wa matasa 6000 da mata masu zaman kashe wando ta hanyar samar musu da aikin yi a cikin jama’a (Labour Intensive Public Workfare, LIPW). Haka kuma, za a ba da tallafin bunkasa sana’o’i ga matasa da mata 8000 masu neman cigaban tattalin arziki.

“A yayin zaɓen waɗanda za su amfana daga wannan shiri, dole ne a yi amfani da ƙa’idar adalci da gaskiya wajen tantance dukkan mutanenmu a mazabu daban-daban.” In ji Gwamna Lawal.

Jama’a na sa ran zaɓen ƙananan hukumomin zai kasance mai mahimmanci wajen ƙarfafa dimokuradiyya da bunkasa cigaban al’umma a Jihar Zamfara, yayin da ake ci gaba da tsara dukkan matakan da za su tabbatar da cewa an gudanar da shi cikin nasara.