Wike ya yi alƙawarin kammala aikin jirgin ƙasan Abuja nan da wata shida

top-news

Ministan Birnin Tarayya Abuja na Najeriya, Nyesom Wike, ya yi alƙawarin magance ɗaya daga manyan matsalolin da mazauna birnin ke fuskanta a ɓangaren sufuri.

Ya bayyana haka yayin wata ziyara da ya kai domin ganewa idonsa aikin gyara tashar sufurin jirgin ƙasan fasinja ta cikin birnin Abuja.

"Sufuri na ɗaya daga cikin ɓangarorin da muke son ingantawa don tabbatar da rage cunkoson ababen hawa a Abuja".

Wike ya ce yana sane da cewa akwai babbar tashar layin dogo ta Abuja da a yanzu ba ta aiki, inda ya bayyana cewa zai tabbatar da ganin ta tashi don fara aiki gadan-gadan.

Ya bayyana cewa akwai ɗumbin ayyuka da ba a kammala ba, kuma abin da mutane suka fi son gani shi ne waɗanda aka kammala kuma suke aiki.

Ya ƙara da cewa babu hikima a fara sabon aiki, ba tare da kammala wanda aka tsoho ba.

"Ina mai tabbatar wa jama'a cewa za mu kammala aikin gyara wannan layin dogo. Sannan kafin mu fara duk wani sabon aiki za mu duba waɗanne wurare ne ke fama da cunkoson ababen hawa don rage samun hakan".buƙatar," in ji shi.

Wannan na ɗaya daga cikin muhimman ayyukan da za mu kammala don ganin an fara amfani da shi nan wata shida"

A cewar ministan birnin tarayyar, "A yanzu haka ma mun tanadi kuɗaɗen da za mu biya wannan kwangila". "Na ba Babban Sakataren birnin tarayya, Adesola Olusade, umurnin tabbatar da biyan ɗan kwangila da ke aikin".

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *