Daga Ibrahim Mohammed Gupa Jnr. – Etsu Gupa Abawa I, Jami’in Yaɗa Labarai
Gwamnatin Kwalejin Bida da ke Jihar Neja, wadda aka kafa tun shekarar 1912 a matsayin Makarantar Sakandare ta Ƙaramar Hukuma (Provincial Secondary School), ta kasance daya daga cikin manyan cibiyoyin da suka bayar da gagarumar gudummawa wajen gina shugabanni a tarihin Najeriya.
Sai dai abin mamaki da ban al'ajabi shi ne irin ci gaban da ɗaliban zangon 1957 zuwa 1962 suka samu. Daga cikin dalibai 24 da suka kammala a wannan lokaci, an samu:
- Shugabanni biyu na ƙasa
- Gwamnoni huɗu
- Ministoci biyu
- Sarakuna huɗu
- Alƙalai uku
- Jakadu huɗu
- Da dama daga cikin su sun zama manyan jami’an soja da shugabanni masu tasiri.
Sunayen Fitattun Ɗaliban da Matsayinsu
-
Janar Ibrahim Badamasi Babangida (Lamba 9) – Ya zama Shugaban Ƙasa na mulkin soja daga 1985 zuwa 1993.
-
Janar Abdulsalami Abubakar (Lamba 16) – Shugaban ƙasa daga 1998 zuwa 1999, wanda ya mika mulki ga gwamnatin farar hula.
-
Janar Gado Nasko (Lamba 21) – Gwamnan Jihar Sokoto.
-
Janar Garba Duba (Lamba 10) – Gwamnan Jihohin Bauchi da Sokoto.
-
Kanal Sani Bello (Lamba 13) – Gwamnan Jihar Kano.
-
Janar Mohammed Magoro (Lamba 3) – Ministan Harkokin Cikin Gida a zamanin Janar Buhari.
-
Brigadier Mohammed Sani Sami (Lamba 23) – Gwamnan Bauchi (1984–1985), yanzu sarki mai daraja a matsayin Sarkin Zuru.
-
Janar Mamman Vatsa (Lamba 6) – Ministan Birnin Tarayya (FCT), wanda daga bisani aka yanke masa hukuncin kisa a 1986 bisa zargin yunkurin juyin mulki a zamanin shugabancin abokinsa Janar Babangida.
Gudummawar Kwalejin a Fannin Shari’a
- Justice Idris Legbo Kutigi – Tsohon Babban Alƙalin Ƙasa
- Justice Jibrin Ndajiwo
- Justice Abdullahi Mustapha
Masu Wakiltar Ƙasa a Ƙasashen Waje
- Jakada James Tsado Kolo (Marigayi)
- Ambassador Buba Ahmed
- Ambassador Yunusa Paiko
- Ambassador Abdulrahman Gara
Shugabanni a Siyasa da Ilimi
- Farfesa Jerry Gana
- Sanata Awaisu Kuta
- Ibrahim Tanko
- Isa Mohammed Waziri
A fannin ilimi kuwa, an haifi fitattun malamai da masana da suka fito daga wannan makaranta irin su:
- Prof. Musa Abdullahi
- Prof. Mohammed Dakota
- Prof. A.I. Kolo
- Prof. M.T.A. Suleiman
Masarautu da Sarauta
Makarantar ta kuma haifar da sarakuna kamar:
- Sarkin Suleja, Malam Auwal Ibrahim
- Sarkin Kontagora, Alhaji Saidu Namaska
- Etsun Lapai
- Sarkin Zuru
Kammalawa
Zangon 1957 zuwa 1962 na Gwamnatin Kwalejin Bida wani gagarumin tarihi ne da ba za a manta da shi ba a tarihin Najeriya. Daga ɗalibai 24 kawai, aka samu shugabanni masu rinjaye a fannoni daban-daban na rayuwa – soja, shari’a, siyasa, jakadanci, da sarauta – abinda ke nuna muhimmancin ilimi da tasirin da irin wannan makaranta ke da shi wajen gina ƙasa.


Comments (0)
No comments yet. Be the first to share your thoughts!