Katsina Ta Kaddamar da Shirin Horas da Matasa Na NYSC Batch A, Stream II Na Shekarar 2025
Zaharaddeen Ishaq Abubakar | KatsinaTimes
Gwamnatin Jihar Katsina ta kaddamar da shirin horas da sabbin ‘yan bautar ƙasa na NYSC Batch A, Stream II na shekarar 2025 tare da kira ga matasa da su ɗauki wannan shekara ta hidimar ƙasa a matsayin gagarumar dama ta gina ƙasa da ciyar da al'umma gaba.
An gudanar da taron kaddamarwar ne a harabar sansanin horas da NYSC da ke kan titin Mani a cikin garin Katsina, ranar Juma'a, 13 ga Yuni, 2025, inda Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Abdullahi Garba Faskari, ya wakilci Gwamna Malam Dikko Umar Radda, PhD.
A yayin jawabinsa ga sabbin ‘yan bautar ƙasa, Faskari ya isar da saƙon gaisuwa daga Gwamna Radda, tare da tabbatar musu da cewa Jihar Katsina na da yanayi mai kyau da mutane masu ɗaukaka da karamci.
“A madadin gwamnatin Jihar Katsina da al’ummar ta, muna yi muku maraba da zuwa. Ku ji kamar kuna gida, domin Katsina jiha ce da ke maraba da NYSC. Za ku samu zaman lafiya da yanayi mai kyau na gudanar da ayyukanku,” in ji shi.
Ya bayyana shirin horaswar a matsayin ginshiki mai muhimmanci da ke shirya matasa a jiki da hankali don fuskantar ƙalubalen bautar ƙasa da kuma rayuwa bayan ta.
“Za a koyar da ku batutuwa da suka shafi tsaro, shugabanci nagari da ci gaban al'umma. Ana sa ran waɗannan za su horar da ku don ku zama masu tasiri a ƙoƙarin gina ƙasa,” in ji shi.
Faskari ya nuna jin daɗinsa kan irin gudunmawar da ‘yan NYSC ke bayarwa a fannonin ilimi, kiwon lafiya da ayyukan cigaban al’umma a jihar.
“Mun gamsu da abin da waɗanda suka gabace ku suka cimma. Ina ƙarfafa ku da ku yi kokarin biyo sahunsu wajen cigaban Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya,” ya ƙara da cewa.
Ya gargadi ‘yan bautar ƙasa da su guji duk wani ɗabi’a da ba ta dace ba, ciki har da nuna bambancin siyasa da addini, tare da kiyaye taken NYSC – Hidima ga Jama’a.
“Ko menene halin da kuka tsinci kanku a ciki, ku ɗauki wannan dama ta bautar ƙasa a matsayin girmamawa da amincewa da ku daga ƙasa,” in ji Faskari, kafin ya ayyana bude shirin horaswar a hukumance.
Kwamishinan NYSC Ya Bayyana Cewa Fiye da 1,200 Sun Yi Rijista a Jihar Katsina
A nasa bangaren, Ko’odinetan NYSC na Jihar Katsina, Alhaji Sa’id Ibrahim, ya bayyana gamsuwa da irin goyon bayan da gwamnatin jihar ke bai wa shirin NYSC a jihar.
“Ina maraba da ku da murna da godiya da kuka samu damar shiga wannan shiri na bautar ƙasa. Muna godiya da halartar Gwamna da kuma goyon bayansa da ba ya ƙarewa ga NYSC a jihar,” in ji shi.
Ya bayyana cewa an yi rijistar ‘yan bautar ƙasa 1,201, maza 696 da mata 505 – zuwa ranar 13 ga Yuni, kuma sun nuna kwazo da shiga sabon muhalli na himma.
“Shirin horaswar nan na da matuƙar muhimmanci domin yana koyar da ladabi, juriya da ɗabi’un kyautata rayuwa a cikin al’umma. Za ku samu horo kan shugabanci, zaman lafiya da ayyukan haɗin kai,” ya bayyana.
Ya ƙarfafa ‘yan NYSC da su rungumi shirin koyon sana’o’i wato SAED (Skills Acquisition and Entrepreneurship Development), inda ya ce hakan zai taimaka musu wajen dogaro da kansu.
"A yau, sana’a ba zaɓi ba ce, dole ce. Mu na ƙarfafa ku da ku halarta da himma a dukkanin ayyukan sansanin,” in ji shi.
Ya kuma gode wa gwamnatin jihar bisa ayyukan da ta gudanar kamar gyaran ɗakunan kwana, samar da kayan zama, da kuma kyautata yanayin rayuwar ma’aikata da ‘yan NYSC a sansanin.
“Wannan tallafi da ku ke bayarwa zai ƙara wa ma’aikata da ‘yan bautar ƙasa kwarin gwiwa da nishaɗi,” ya ƙara da cewa.
Babban Jojin Jihar Katsina, Mai Shari’a Musa Danladi Abubakar, ne ya jagoranci rantsar da sabbin ‘yan NYSC, inda ya karanta musu rantsuwar biyayya ga ƙasa, alamar shigarsu cikakken mataki na bautar ƙasa.