Kungiyar NGGT Ta Karrama Daraktan KASSAROTA

 Kan Gagarumar Gudunmawar da Yake Bayarwa Kungiyar Network for Good Governance and Transparency (NGGT) ta karrama wasu manyan jiga-jigai a....

Katsina City News February 06, 2025  ·  12:00 AM
| 1,355 Views

 Kan Gagarumar Gudunmawar da Yake Bayarwa


Kungiyar Network for Good Governance and Transparency (NGGT) ta karrama wasu manyan jiga-jigai a Jihar Katsina bisa gudunmawar da suke bayarwa ga ci gaban al'umma. Taron karramawar, wanda aka gudanar a dakin taro na Katsina State Secretariat Complex, ya samu halartar manyan baki ciki har da Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, da Darakta Janar na Hukumar KASSAROTA, Major Garba Yahya Rimi (Rtd.), wanda kuma shi ne Tafidan Kauran Katsina, tare da wasu fitattun mutane daga fadin jihar.

Advertisement

Kungiyar NGGT ta karrama Daraktan KASSAROTA, Major Garba Yahya Rimi, bisa kokarin da yake yi wajen habaka ci gaban matasa da kuma inganta ayyukan hukumar KASSAROTA a jihar. Haka nan, wasu daga cikin jami'an da suka goyi bayan wannan karramawa sun hada da ASTC A. Muntari, Kwamandan NGGT na shiyyar Katsina, da kuma jami’in hulda da jama’a na hukumar, Abubakar Marwana Kofar Sauri.

Rahoto: PRO

Abubakar Marwana Kofar Sauri

Written by

Katsina City News

Katsina City News is a journalist and correspondent at Katsina Times — covering local, national and international news with a focus on Northern Nigeria.

Comments (0)

No comments yet. Be the first to share your thoughts!

Leave a Comment

What is 9 + 7?