RA'AYIN JARIDAR PUNCH: Kisa ba bisa doka ba: Tinubu, ka kawo karshen rashin hukunta Sojoji, DSS

top-news

RA’AYIN JARIDAR THE PUNCH
11 ga Satumba, 2023

Shekaru 24 da fara mulkin farar hula, kashe-kashen ba bisa ka'ida ba na karuwa da kuma tauye hakkin dan Adam da dimokuradiyya a Najeriya. A ranar Alhamis din da ta gabata ne ’yan sanda a babban birnin tarayya suka kwantar da wata zanga-zangar nuna adawa da wani rahoto da ke cewa jami’an Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) sun kashe wani mai shagon kayan kawa tare da jikkata wasu da dama. Kodayake daga baya ta bayyana cewa, wanda aka ce an kashe din ya tsira daga harbin, amma hakan bai kawar da fushin jama'a ba ko kuma kawar da gaskiyar zartar da hukuncin kisa da jami'an Hukumar ke yi. Ya kamata Shugaba Bola Tinubu ya sanya rashin yarda da irin wannan nuna fin karfin doka, kuma ya kawar da wannan mummunar dabi'a.

’Yan Najeriya na dandana kudarsu a hannun makasa da sunan Hukuma da wadanda ba su ba. Al’amuran kashe-kashe ba bisa ka’ida ba na yawan faruwa a fadin kasar nan tare da bata rai, wani lokaci jami’an soji da jami’an DSS da ’yan sanda masu wuce-gona-da-iri suke aikatawa.

Haka zalika jami’an hukumar kwastam ta Najeriya, hukumar shige da fice ta kasa, jami’an tsaron farin kaya, jami’an tsaron farin kaya, da jami’an ’yan banga sukan far wa fararen hular da ba su ji ba, ba su gani ba.

Lamarin da ya faru a babban birnin Tarayya, FCT, yana nuna rashin bin doka daga masu kayan sarki da ke yawan faruwa.  Shaidu sun ce wani kwastoma ne ya kawo jami’an DSS zuwa shagon sayar da rigunan kawa bisa zargin kin kai wasu kaya a ranar da aka amince. Wani zazzafan cece-kuce tsakanin bangarorin biyu ya kawo karshe ne sa’ilin da jami’an DSS suka yi harbin bindiga domin tarwatsa magoya bayan mai shagon kayan adon, wanda a lokacin harsashi ya same shi.  Daga baya hukumar ta DSS ta amince cewa jami’anta sun fuskanci hari ne daga “gungun ’yan zanga-zanga,” amma ba ta yi gamsasshen bayanin meye ruwansu da wani lamari na farar hula ba.

A watan da ya gabata ne a Legas wasu sojoji da ba a san ko su waye ba suka tare wani direba mai suna Lawal da ke kan hanyarsa ta kai mota Abuja, suka kai shi unguwar Iyana-Ipaja inda suka harbe shi har lahira. Haka kuma, wani mataimaki ga wani Sanata mai suna Olamilekan Adeola, wasu sojoji dauke da makamai sun kama shi a unguwar Ojodu, amma daga baya aka tsinci gawarsa an jefar a kusa da Oshodi.

A watan Maris din da ya gabata ne dai wani jami’in DSS ya kashe wani mutum a Ogidi da ke Karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra, wanda matarsa ta haifo jariri a lokacin da jami’an tsaro suka bi sahun wani mutum da ake zargi da aikata laifi wanda ya shiga gidansa. Wani ma’aikacin DSS mai sakaci, mai suna Bamidele, a cikin watan Disamba 2021, ana zargin ya kashe wani matashi mai shekaru 21 mai neman aiki, Temitope Johnson, ta hanyar “harsashi da ya kauce hanya” a Owode Ede, jihar Osun.

An bayar da rahoton cewa sojoji masu farautar mambobin haramtacciyar kasar Biafra a Orlu, jihar Imo, a watan Afrilun 2022, sun bude wuta, tare da kashe wasu da ba su ji ba, ba su gani ba.

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana kisan gilla, ko kisa ba tare da shari'a ba, a matsayin kisan da gangan aka yi wa mutum ba tare da wata doka ba da ta taso daga tsarin shari'a. Lallai, daga cikin duk wani haƙƙin ɗan Adam da aka amince da shi, in ji mai ba da rahoto na musamman na Majalisar Dinkin Duniya kan kisan gilla, 'yancin rayuwa shi ne mafi muhimmanci. Ya kara da cewa, "Ba tare da mutunta 'yancin yin rayuwa ba, babu wani hakkin dan Adam da za a iya karewa."

Amma wasu jami’an tsaron Najeriya ba su damu ba. A cikin shekaru 10 kafin 2021, Cibiyar Dimokuradiyya da Ci gaba, wata cibiyar bincike ta bayyana cewa, jami'an tsaro sun kashe mutane 13,241 ba tare da shari'a ba. Kungiyar Amnesty International ta ce 'yan sanda da sojoji sun kashe mutane 115 a watan Maris zuwa Yunin 2021 a Kudu maso Gabas. A cikin shekara zuwa Yuni 2020, 'yan sanda sun kashe farar hula 91.  UNSR ta ce jami’an tsaro sun kashe ‘yan Najeriya 261 ba tare da shari’a ba a shekarar 2019.

A ranar Kirsimeti 2022, wani dan sanda ya kashe Bolanle Raheem, wata lauya mai juna-biyu mai shekaru 41 a karkashin gadar Ajah, Legas, ba gaira ba dalili. An kashe Usman Bala mai shekaru 16 a watan Satumban 2022 lokacin da wasu jami'an 'yan sanda suka mamaye wata al'umma a Karamar hukumar Jos ta Arewa, jihar Filato.

 Baya ga irin wadannan kashe-kashen ba bisa ka'ida ba kan neman cin hanci da kuma 'yan rashin jituwa, kisan kiyashi a wasu lokutan ma na faruwa. Sojojin Najeriya sun kashe 'yan’uwa musulmi na Harkar Musulunci guda 347 a Najeriya a watan Disambar 2015 bayan wani hari da suka kai musu a wurarensu da ke Zaria a jihar Kaduna. Lauyan kare hakkin jama’a, Femi Falana, ya ce adadin ’yan Shi’a 492 ne sojoji da ’yan sanda suka kashe ba bisa ka’ida ba tsakanin shekarar 2014 zuwa 2018.

A watan Disambar 2022 ne sojojin ruwan Najeriya suka caka wa Hezekiah Abiona, ASP, wuka har lahira bayan gardama kan karya dokar tuki da wani sojan ruwan ya yi.

Tun lokacin da aka ba su izinin ɗaukar bindigogi, ma'aikatan NIS da NCS sun salwantar da rayukan marasa laifi. A watan Yulin bana, an zargi wani jami’in shige da fice mai suna ‘Lamba,’ da harbe Jacob Bamgbola, wanda ya shirya zanga-zangar da matasa suka yi a Idigbo, Yewa, jihar Ogun, kan karbar kudin da jami’an NIS suke yi a garin kan iyaka na Idi-Iroko. A wannan watan ne a Jibia, jihar Katsina, harsashin jami’in NIS kuma ya kwantar da Raji Muhammad bisa zargin kin bayar da cin hancin Naira 2,000 a kan iyakar Najeriya da Jamhuriyar Nijar.

Rahotanni sun bayyana cewa, jami’an hukumar kwastam sun yi ta salwantar da rayuka a yankunan kan iyaka da kuma kasuwannin cikin gida. Wannan ne ya sa Gwamnan Katsina a lokacin, Aminu Masari ya yi barazanar kai karar hukumar NCS. A wani lamari da ya faru a shekarar 2022, jami’ai sun kashe mutane 10 tare da raunata wasu 13 a Jibiya, da sunan wai suna neman ’yan sumoga.

Majalisar dattawa ta kafa wani kwamiti na wucin-gadi a shekarar 2021, biyo bayan rahotanni masu zafi da aka samu daga hare-haren da hukumar kwastam ta sha kaiwa a garuruwan jihohin Ogun, Oyo, Katsina da sauran jihohi.  Majalisar wakilai ta kuma fara gudanar da bincike kan kashe-kashen da hukumar kwastam ke yi wa mazauna garin Iseyin na jihar Oyo.

Kuma a watan Yulin da ya gabata ne kafafen yada labarai suka bayar da rahoton harbin wani dan kasuwa mai suna Kelechi Amadi mai shekaru 25 da haihuwa a garin Umuahia na jihar Abia, wanda jami’in NSCDC da aka yi zargin ya nemi cin hancin Naira 2,000 “don man fetur,” kuma suka tafi da shi, amma sai dai aka ga an jefar da gawarsa daga baya a asibiti.

Bai kamata Najeriya ta ci gaba da tafiya a kan wannan hanya ta rugujewa ba. Tuni aka sanya kasar nan a matsayin na 15 mafi rauni (daga cikin kasashe 177) a cikin alkalumna kasashe masu rauni na 2023, kisan gilla da jami'an jihar ke yi na kara dagula lamarin. Yayin da ake fama da matsalar rashin tsaro, inda wasu da ba na gwamnati ba suka kashe mutane 4,545 tare da yin garkuwa da wasu 4,611 a shekarar 2022, bisa ga bayanan da Cable Index ta tattara, kisan da jami’an tsaron kasa suke yi abu ne mai tsauri na biyu ke nan.

Mummunan kashe-kashe da cin zarafi da jami'an 'yan sanda suka yi ne ya janyo zanga-zangar matasa ta #EndSARS ta shekarar 2022 da ta kai ga asarar rayuka a Lekki Tollgate Plaza, Legas, wanda har yanzu ba a bar cece-kuce a kai ba, amma kwamitin da aka kafa ya bayyana raunata mutane 48, yayin da sojoji da 'yan sanda suka tabbatar da kashe mutum tara.

Dakatar da kashe-kashe da al'adar rashin adalci da ke haifar da hakan na bukatar kwakkwaran manufa ta siyasa da daukar mataki na Shugaban kasa da wadanda yake nadawa a madafun gwamnati. Ana ci gaba da kashe-kashe da tsare mutane ba bisa ka'ida ba da azabtarwa domin kadan ne daga cikin wadanda suka aikata laifin aka taba gurfanar da su a gaban kotu. Wannan lamari ne na hakika, musamman ga sojoji da dakarun sa-kai. Ba a yi wani hukunci kan kisan kiyashin da sojoji suka yi wa fararen hula a Odi, Jihar Bayelsa, 1999; da kuma a Zaki Biam, Jihar Benue, 2001, inda mutane 900 da mutane 200 suka mutu.

A baya-bayan nan, bayan shekaru da dama da aka shafe ana tafka ta’asa, rundunar ’yan sandan Najeriya ta fara daukar mataki kan jami’anta marasa bin doka da oda, wadanda ke kashewa, da raunata wasu, da karbar kudi, da kuma cin zarafin ’yan Najeriya da ba su ji ba, ba su gani ba.

Sai dai sojoji da DSS da sauran su ba su bi sahunsu ba. Jami’ansu da ke kashe-kashe ba tare da bin ka’ida ba da kuma ta’asa ga fararen hula sukan tsere wa gurfana gaban kotu. Misali, samame da kashe ’yan Shi’a 347 da aka yi bai samu bincike da nufin gurfanar da wadanda suka aikata shi daga gwamnatin tarayya ba; Sojojin da suka kashe dan sanda a Ojo da ke jihar Legas, ba a gano ko su wanene ba, balle kuma a gurfanar da su a gaban kuliya, sannan kuma wadanda suka kashe ’yan sanda domin ceto wani mai garkuwa da mutane, Hamisu Bala, wanda aka fi sani da ‘Wadume,’ a jihar Taraba, sun yi tafiyar su cikin ‘yanci, yayin da Bala ya samu hukuncin dauri.

Don haka dole ne a fara yin gyare-gyare. Dole ne a daidaita ƙa'idodin aikin kai farmaki da jami’an tsaro ke yi kan fararen hula don dacewa da ka'idojin dimokuradiyya, bin doka da mutunta haƙƙin ɗan Adam. Ya kamata a aiwatar da shawarwarin da kwamitoci daban-daban na kawo sauyi ga 'yan sanda suka bayar a baya. Waɗannan sun haɗa da shirin shekara biyar a 2000, Rahoton Tamuno 2002, Rahoton Dandami na 2006, shawarwari 125 na Rahoton MD Yusuf na 2008, da makamantan rahotanni a 2010 da 2012.

Ya kamata Tinubu ya fara aikin canza Hukumomin ’yan sanda da sojoji da sauran jami’an tsaro zuwa Hukumomi na jin kan  jama’a tare da yaye su daga kiyayyar da suke yi wa farar hula da aka dauke su aiki saboda su, kuma ake horar da su, ana biyan su su ba su kariya.

Dole ne manyan hafsoshin soji na kasa da na sama da na ruwa su yi wa rundunar garambawul. Ya kamata a daina karyatawa da ba da kariya ga ma'aikatansu da suka yi kisa ko aukawa jama’a a wajen bariki. Ba al'adar kwarai ba ne sojoji a tsarin dimokuradiyya a same su suna tafka ta'asa ga fararen hula.

Ko da a cikin yanayin yaƙi, akwai ƙa'idodin da aka yarda da su a duniya na huldatayya. A karkashin dokar Majalisar Dinkin Duniya da kuma dokokin Hague da Najeriya ta rattaba hannu a kai, sojojin mamaya da sauran su, an haramta musu harin ramuwar gayya, da hukunta jama’ar gari, ko barnatawa ko kwace dukiyoyi, kuma duk wanda ake zargi da aikata laifi irin wannan dole ne a yi masa shari’a ta gaskiya.

An gurfanar da wani sojan Isra'ila, Elor Azaria, wanda ya bindige wani Bafalasdine da ya kai hari, inda ya kashe shi, saboda wanda aka kashe din yana nan kasa amma ya harbe shi. A bana, a cikin yakin da take yi da ’yan ta’addan miyagun kwayoyi, Mexico na tuhumar wasu sojoji da laifin aiwatar da hukuncin kisa kan mutane 10. Hukumomin Burtaniya sun kaddamar da bincike kan zargin kashe 'yan Afganistan sama da 80 a tsakanin shekarar 2010-2013 da manyan kwamandojin rundunarta na musamman na Air Service suka yi. Ku fa tuna cewa Biritaniya ta yi asarar jimillar sojoji 457 a Afghanistan, sama da 100 daga cikin su a shekarar 2009/10 kadai, a cewar majalisar dokokin Birtaniya.

Amma waɗannan laifuka suna bunƙasa a nan ne saboda ba mummunan sakamako ga masu aikata su. Sojoji da jami’an DSS suna ci gaba da yi kamar sun fi karfin doka, kuma suna watsi da umarnin kotu. Rashin hukunta su ya kai wani mummunan matsayi a karkashin gwamnatin da ta shude ne ta Muhammadu Buhari.

Tinubu yana da hakki na gaggawa na jajircewa kan dawo da su kan turbar da ta dace. Daga yanzu, ya kamata a sami hukunci mai ƙarfi da gaggawa na rashin bin doka da oda daga jami'an tsaron gwamnati.

Kisan gilla ba bisa doka ba, shi ma kisan kai ne; babu wani ko wata hukuma da ke da hakkin daukar ran wani ba tare da hukuncin kotu ba, kuma sai bayan an yi shari’a ta gaskiya da aiki, ko kuma yafe hakkin daukaka kara zuwa kotun koli na kasar. Sojoji da DSS da sauran jami’an tsaro da suka kashe wani ko wasu, to a mika su ga ’yan sanda domin bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu. Mai da irin wadannan laifuka a matsayin na cikin gidan hukumomin da za a iya share su a karkashin kafet ya saba wa doka kuma ba za a amince da shi ba.

Ya kamata ’yan majalisar tarayya da na jihohi su nuna damuwarsu da hanzari a duk lokacin da jami’an tsaro suka kashe farar hula ba tare da shari’a ba ko kuma suka tursasa su. Ya kamata Majalisar Dokoki ta kasa ta sake duba dokokin da ake da su, sannan ta kafa tsauraran hukuncin kan irin wannan kisa daga jami’an tsaro.

Tinubu ya kamata ya tafiyar da gwamnati mai cikakken bin tsarin dimokuradiyya tare da tabbatar da cewa dukkan hukumomin tsaron kasa sun ba da cikakkiyar mutunta doka da hakkin dan Adam.

Mafi asali daga cikin wadannan shi ne 'yancin rayuwa; dole ne a kiyaye shi ko ta halin kaka daga karkatar da shi daga bangaren jami’an tsaro na kasa da wadanda ba na kasa ba.

Kabarin bai-daya da aka yi wa 'yan'uwa musulmi 347 a Mando a kisan kiyashin da sojoji suka yi a Zariya a 2015. 
Ga kuma gidan Malam da Husainiyya da suka rusa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *