Gwamna Radda a Kwana 100 na Mulkin jihar Katsina

top-news

Katsina

A cikin kwana 100, abubuwan arzikin da Gwamnatin Jihar Katsina ta yi karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda, sun hada da tunkarar matsalar tsaro, inda ya amince da kashe kudade kimanin naira miliyan dubu 7.8.

Sannan Malam Radda, ya jagoranci samar da fili na wucin gadi wanda za a kafa Jami’an Kiwon Lafiya ta Gwamnatin Tarayya a Karamar Hukumar Funtua ta Jihar Katsina.

Bayan haka, Gwamnan ya ba da umarnin sayen shinkafa, inda za a kashe naira miliyan dubu biyu da Gwamnatin Tarayya ta baiwa jihohi.

Radda, ya ba da aikin fadada gadar Kofar Kaura da ta fara zama barazana, musamman ambaliyar ruwa; inda yanzu haka an kusa kammala ayyukan wannan gada.

Haka kuma, gwamnan ya ba da umarnin a fitar da miliyoyin nairori, domin daukar nauyin wadanda iftila’in ‘yan bindiga ya shafa a Jihar Katsina.

Abu na farko da Gwamnan Jihar Katsinan, Malam Dikko Umar Radda ya fara shi ne, cire masu rike da mukaman siyasa wadanda ya gada daga tsohon Gwamna Aminu Bello Masari.

Sai kuma, yadda Gwamna Raddan ya dakatar da manyan sakatarori daga mukamansu kafin daga baya ya kafa wani kwamiti da zai shirya jarrabawa ga duk wanda ke san zama Babban Sakatare.

Da yawa daga cikinsu, sun fadi wannan jarrabawa da aka ce an dauko wani kwararre daga Jihar Barno, domin shiryawa.

Haka kuma, gwamnan ya yi tafiye-tafiye har sau goma sha daya zuwa Abuja, sannan ya fita kasashen waje sau uku, inda yanzu haka ya bar kasar kusan kimanin kwana goma.

Har ila yau, Malam Dikko Radda ya ba da umarnin Kananan Hukumomin Jihar Katsina 34, su sayi masara domin raba wa jama’a, sai dai har gobe jama’a na tambayar nawa aka kashe wajen sayen wannan masara, batun da har gobe babu amsa daga bangaren gwamnatin

Bayan haka, Gwamnatin Radda ta dawo da dokar hana hawa babur  a wasu garuruwa da ke fama da matsalar tsaro, batun da masana ke cewa, dokar ba ta haifar da da mai ido ba.
Cirowa daga Jaridar Leadership Hausa