Ministan Tsaro Ya Ziyarci Rundunonin Soji a Katsina, Yana Tabbatar da Goyon Bayan Gwamnatin Tinubu

top-news

Zaharaddeen Ishaq Abubakar, Katsina Times 

Ministan Tsaron Najeriya, Mohammed Badaru Abubakar, ya ziyarci bangarorin tsaron soji a Katsina, inda ya tabbatar wa jami'ai da sojoji cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na daukar matakan horaswa da samar da kayan aiki don inganta shirye-shiryen yaki da 'yan ta'adda.

Da yake jawabi ga Operation Hadarin Daji a dandalin 213 Forward Operating Base, Katsina, Ministan ya yaba da nasarorin da Shugaba Tinubu ya samu wajen yaki da 'yan ta'adda da laifuka masu alaka da su. Ya bukaci sojojin da su ci gaba da yaki da 'yan ta'adda da 'yan bindiga, yana yaba musu bisa sadaukarwa da jajircewarsu.

Dangane da harin da ya faru kwanan nan wanda ya yi sanadiyyar kisan sojoji a jihar Abia, Ministan ya tabbatar da kudurin gwamnatin na gurfanar da masu laifin gaban shari'a da kuma hana irin wannan abu faruwa nan gaba.

Air Commodore G.I. Jibia, Kwamandan Sashin Jiragen Sama na Operation Hadarin Daji, ya gode wa Ministan bisa ziyarar, yana mai cewa hakan zai kara wa sojoji kwarin gwiwa.

Tun da farko, Ministan ya gudanar da tattaunawa tare da jami'ai da sojojin hedkwatar Brigade ta 17 ta Sojojin Najeriya da Sector 2 Joint Task Force Operation Hadarin Daji, Katsina, domin tantance shirinsu na fuskantar barazanar tsaro a yankin.

Ministan ya kuma ziyarci Cibiyar Lafiya ta Sojojin Najeriya a Katsina, inda ya jajanta wa sojojin da suka samu raunuka yayin ayyukan yaki.

NNPC Advert