Gwamnatin Katsina Ta Jaddada Goyon Baya Ga Shirin Hana Tsattsauran Ra'ayi

top-news

Zaharaddeen Ishaq Abubakar, Katsina Times

A cikin wani yunkuri na ƙara azama kan yaki da ta'addanci a arewa maso yammacin Najeriya, wata tawaga daga Abuja ta kai ziyarar girmamawa ga Gwamnan Jihar Katsina, Dr. Umar Dikko Rada. Tawagar, karkashin jagorancin Amb. Mairo Musa Abbas, Daraktar Sashen Hana da Magance Tsattsauran Ra'ayi a Cibiyar Yaki da Ta'addanci ta Kasa, ta nemi goyon bayan Gwamnan don ci gaba da aiwatar da shirin hana tsattsauran ra'ayi a yankin.

Tawagar ta isar da sakon gaisuwar mai ba da shawara kan tsaro na ƙasa, Tsohon Mataimakin Sufeto-Janar na 'Yan Sanda, Mallam Nuhu Ribadu. A yayin ziyarar, Amb. Abbas ta yi nuni da muhimman ayyuka da Ofishin Mai Ba da Shawara Kan Tsaro na Kasa (ONSA) ya amince da su a shekarar 2022 kuma asusun Global Community Engagement and Resilient Fund (GCERF) ke ɗaukar nauyi. Waɗannan ayyuka suna karkashin kulawar kungiyoyi uku: Action Aid a Kano da Kaduna, North East Youth Initiative for Development (NEYIF) a Sakkwato, da Women Environmental Programme (WEP) a Katsina.

Amb. Abbas ta jaddada buƙatar samun goyon bayan gwamnati don tabbatar da dorewar waɗannan ayyuka. Ta yabawa Gwamna Rada bisa kafa Hukumar Kula da Tsaron Al'umma ta Jihar Katsina, wadda ta ƙara inganta kariyar farar hula da tsaron jihar.

Ɗaya daga cikin ayyukan da aka yi nuni da shi shi ne shirin WEP na "Karfafa Yaki da Tsattsauran Ra'ayi (SAVE)," wanda aka gudanar tare da haɗin gwiwar Murna Foundation. Wannan shiri, wanda ya shafi daga 2022 zuwa Yuni 2024, ya kai ga mutane fiye da 30,000 a kananan hukumomi huɗu: Funtua, Dutsin-Ma, Musawa, da Jibia. Shirin ya haɗa da ba wa samari da 'yan mata 400 horo kan sana'o'i da ƙarfafa gwiwa, da kuma ba wa mata tallafin lamuni na kasuwanci.

Duk da waɗannan ƙoƙari, jihar Katsina na ci gaba da fuskantar ƙalubale masu yawa. Kididdigar Multidimensional Poverty Index na nuna cewa kusan kashi 72.7% na al'ummar jihar, wato mutane miliyan 6.92, na fama da talauci mai fadi. Wannan mawuyacin hali na tattalin arziki, tare da ƙaruwar ayyukan kungiyoyin tsattsauran ra'ayi, yana ƙara nuna gaggawar buƙatar neman goyon bayan gwamnati.

A ƙarshe, tawagar ta sake jaddada buƙatar samun cikakken goyon bayan gwamnatin Jihar Katsina don tabbatar da dorewar ayyukan da GCERF ke ɗaukar nauyi da kuma ƙarfafa gwiwar al'ummomi wajen yaki da tsattsauran ra'ayi.

Sakataren Gwamnatin jihar Katsina a madadin Gwamnan jihar Katsina ya tarbi tawagar tare da wakiltar Gwamnan, inda ya bayyana jin dadi tare da gamsuwa ga tsare-tsaren waɗannan muhimman ayyuka. Barista Abdullahi Garba Faskari ya bayyana irin ƙoƙarin gwamnatin Jihar Katsina a kan magance matsalolin tsaro ta hanyoyin daban-daban.

Taron da aka gudanar a Ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina dake babban sakatariyar jihar Katsina ya samu halartar Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida a Jihar Katsina, wakilan kungiyoyin farar hula, jami'an tsaro, 'yan jarida da sauransu.

NNPC Advert