Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), reshen Jami’ar Umaru Musa Yar’adua (UMYU), ta taya Gwamnan Jihar Katsina murna bisa ba shi digirin girmamawa da jami’ar ta yi.
A wata sanarwar manema labarai da kungiyar ta fitar a ranar Litinin, ASUU-UMYU ta bayyana cewa ba da digirin girmamawar wata shaida ce ta jagoranci, jajircewa wajen bunkasa ilimi, da kuma gudummawar da gwamnan ya bayar wajen cigaban Jihar Katsina da Najeriya baki daya.
Kungiyar ta ce jami’ar ta amince da kokari da manufofin gwamnan da suka taimaka wajen karfafa bangaren ilimi a karkashin gwamnatinsa.
ASUU-UMYU ta yaba musamman da manufar gwamnan ta ba wa fitattun daliban da suka fi kowa kwarewa a kowane sashe na jami’ar aikin yi kai tsaye bayan kammala karatu. Kungiyar ta ce wannan tsari na karfafa kwazo da hazaka a tsakanin dalibai tare da zaburar da su su yi kokarin yin fice a fannonin karatunsu.
A cewar sanarwar, manufar ta kuma nuna yadda gwamnan ke mutunta cancanta, karfafa matasa da bunkasa jarin al'umma.
Har ila yau, kungiyar ta bayyana gwamnan a matsayin jagora na musamman a fannin cigaban ilimi, tana mai cewa shi ne gwamnan jiha na farko a Najeriya da ya amince da aiwatar da sabon tsarin albashi ga ma’aikatan jami’o’i, wanda aka fara aiwatarwa a jami’o’in tarayya a watan Janairu, 2026.
ASUU-UMYU ta ce wannan mataki na nuna hangen nesa, jarumtaka da kulawa ga walwalar ma’aikatan jami’o’i, tare da kafa abin koyi ga sauran jihohi.
Kungiyar ta kara da cewa kasancewar gwamnan tsohon malami ya taimaka wajen tsara manufofinsa da kuma jajircewarsa wajen karfafa cibiyoyin ilimi.
ASUU-UMYU ta ce ta dauki ba da digirin girmamawar a matsayin abin da ya dace kuma ya cancanci yabo, tare da sake jaddada aniyarta ta ci gaba da bai wa gwamnatin jihar goyon baya.
Sanarwar ta samu sa hannun Shugaban ASUU-UMYU, Dakta Murtala Abdullahi Kwara.