APC Ta Maye Gurbin Uzodimma Da Masari A Shugabancin Kwamitin Taron Ƙasa

uploads/images/newsimages/KatsinaTimes06022026_164625_FB_IMG_1770395714298.jpg



Daga Wakilinmu | KatsinaTimes

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sanar da sauyi a shugabancin Kwamitin Shirya Babban Taron Ƙasa na jam’iyyar, inda ta maye gurbin Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, da tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari, a matsayin shugaban kwamitin.

An bayyana wannan mataki ne a ranar Alhamis bayan kammala taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NWC) na jam’iyyar da aka gudanar a Abuja, a wani bangare na shirye-shiryen babban taron ƙasa da APC ke shirin gudanarwa.

Majiyoyi a cikin jam’iyyar sun bayyana cewa Gwamna Uzodimma, wanda shi ne tsohon shugaban kwamitin, an mayar da shi matsayin Ma’aji (Treasurer) na kwamitin shirya taron, yayin da Masari zai jagoranci dukkan ayyukan tsarawa da aiwatar da shirye-shiryen taron ƙasa.

Shugabancin APC ya ce an sake fasalin kwamitin ne domin ƙara inganta tsari, ƙarfafa haɗin kai, da tabbatar da gudanar da taro cikin nasara, adalci da kwanciyar hankali.

Aminu Bello Masari, wanda ya taba zama Kakakin Majalisar Wakilai ta Ƙasa kuma gwamna na wa’adi biyu a Jihar Katsina, na daga cikin fitattun jagororin APC da ake ganin yana da kwarewa mai zurfi a harkokin jam’iyya da siyasar ƙasa.

Ana sa ran babban taron ƙasa na APC zai taka muhimmiyar rawa wajen tsara shugabanci da alkiblar jam’iyyar, musamman gabanin manyan zaɓukan da ke tafe.

Shugabannin jam’iyyar sun tabbatar wa mambobi da masu ruwa da tsaki cewa wannan sauyi ba zai kawo tangarda ga shirye-shiryen taron ba, illa ma zai ƙara inganta haɗin kai da nagartar gudanarwa yayin da ranar taron ke ƙara matsowa kusa.

Follow Us