An Ɗage Dokar Hana Zirga-zirga A Kano

top-news

Rundunar 'yan sanda a jihar Kano ta sanar da ɗage dokar hana fita ta tsawon sa'a 24, da aka sanya a jihar.

Mai magana da yawun rundunar, SP Abdulahi Haruna Kiyawa ne ya sanar da haka a wani sako da ya wallafa a shafin Facebook.

A ranar Laraba ne dai rundunar ƴan sandan Kano ta sanya dokar bayan yanke hukuncin kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen gwamna, da ya soke nasarar Abba Kabir Yusuf, tare da ayyana Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin halastaccen gwamna.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *