Gwamnatin Katsina Ta Kaddamar da Kwamitin Almajirai Don Inganta Iliminsu

uploads/images/newsimages/KatsinaTimes19032025_182055_FB_IMG_1742408163497.jpg



Zaharaddeen Ishaq Abubakar | Katsina Times
Katsina, Najeriya – 19 ga Maris, 2025

Gwamnatin Jihar Katsina ta kafa kwamitin musamman domin duba tsarin karatun almajirai tare da bullo da sabbin hanyoyin inganta iliminsu da jin daɗinsu. An kaddamar da kwamitin ne a ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar (SGS), inda ya wakilci Gwamna Malam Dikko Umar Radda, PhD.

A yayin kaddamar da kwamitin, Sakataren Gwamnati, Abdullahi Garba Faskari, ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na ci gaba da inganta ilimi, musamman ta hanyar daidaita tsarin karatun almajirai da na zamani. Ya bayyana cewa kwamitin zai mayar da hankali wajen nazarin matsalolin da almajirai ke fuskanta da kuma bayar da shawarwari masu inganci don kyautata karatunsu.
Professor Abdulhamid Ahamed Shugaban Kwamitin 

Shugaban kwamitin, wanda kuma shi ne Kwamishinan Cigaban Karkara da Zamantakewa, Farfesa Abdulhamid Ahamed, ya gode wa gwamnatin jihar bisa amincewa da su domin gudanar da wannan muhimmin aiki. Ya tabbatar da cewa za su yi aiki tukuru don cimma manufofin da aka sanya a gaba.

"Mai girma gwamna, bisa la’akari da mutanen da aka zabo a wannan kwamitin, za a fahimci muhimmancin da ake bai wa wannan aiki. Mun karɓi wannan nauyi gaba ɗaya, kuma za mu yi aiki da gaskiya da kishin ƙasa," in ji shi.

Farfesa Abdulhamid ya kuma bayyana cewa, duk da ƙalubalen da ke akwai, kwamitin zai fitar da cikakken rahoto cikin gaggawa.

"Ina tabbatar muku da cewa za mu yi iya bakin kokarinmu don ganin mun cimma nasarar da aka dora mana. Muna fata sakamakon wannan aiki ba zai amfanar da Jihar Katsina kaɗai ba, har ma da sauran jihohin Najeriya," ya ƙara da cewa.

Kwamitin zai gabatar da shawarwari kan yadda za a inganta tsarin karatun almajirai tare da daidaita shi da bukatun zamani, ba tare da barin al’adun da addininsu ya shimfiɗa ba.

Follow Us