Gwamnatin Kano ta yi watsi da ƙudirorin dokar haraji

Gwamnatin jihar Kano ta yi watsi da ƙudirorin dokar haraji da ake ta cece-kuce s kan shi tsawon watanni a....

Katsina City News January 02, 2025  ·  12:00 AM
| 1,753 Views
Gwamnatin jihar Kano ta yi watsi da ƙudirorin dokar haraji da ake ta cece-kuce s kan shi tsawon watanni a Nijeriya.

Gwamnatin, ta bakin mataimakin gwamnan, mataimakin gwamna, Aminu Abdussalam Gwarzo, a wajen bikin sabuwar shekara da ya gudana a filin Mahaha a Kano, ta baiyana matsayin ta cewa ba ta tare da waɗannan ƙudirori.

A wata sanarwa da kakakin mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shuaibu ya fitar, Gwarzo ya ce kudirorin dokar haraji ba shi ne mafita a halin matsin tattalin arziki da ake fama da shi a kasar.

Gwarzl ya kara da cewa gwamnatin jihar ba ta goyon bayan ƙudirorin, inda ya yabawa al'ummar jihar Kano bisa juriya da hakuri da halin kunci rayuwa da ake fama da shi a ƙasar.
Daily Nigeria Hausa 

Advertisement

Written by

Katsina City News

Katsina City News is a journalist and correspondent at Katsina Times — covering local, national and international news with a focus on Northern Nigeria.

Comments (0)

No comments yet. Be the first to share your thoughts!

Leave a Comment

What is 4 + 6?