An kashe kasurgumin ɗan ta’adda, Sani Rusu, a Zamfara

Sojojin Bataliya ta 1 a Arewa Maso Yamma, ƙarƙashin 'Operation Fansan Yamma', sun kashe wani kasurgumin ɗan ta’adda, Sani Rusu,....

Katsina City News January 06, 2025  ·  12:00 AM
| 2,072 Views
Sojojin Bataliya ta 1 a Arewa Maso Yamma, ƙarƙashin 'Operation Fansan Yamma', sun kashe wani kasurgumin ɗan ta’adda, Sani Rusu, a jihar Zamfara.

Sojojin sun kuma yi nasara a wasu ayyuka daban-daban da suka yi kan ƴan ta’adda a jihar tare da kwato makamai.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da jami'in yaɗa labarai na cibiyar yaɗa labarai ta haɗin gwiwa na Operation Fansan Yamma, Laftanar Kanar Abubakar Abdullahi, ya fitar a Gusau a yau Litinin.

Ya ce “A ranar 4 ga Janairu, sojojin sun gudanar da sintiri zuwa garin Bamamu a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, inda su ka yi artabu da ƴan ta’adda a yankin.

“Bayan haka, an kashe wani kasurgumin shugaba a cikin su, Sani Rusu, a yayin wannan artabu.

“Har ila yau, a wannan rana, yayin wani kwanton bauna da aka gudanar bisa sahihan bayanan sirri kan ayyukan ƴan ta’adda a Kwanar Jollof a ƙaramar hukumar Shinkafi, sojojin sun kashe wasu ƴan ta’adda, yayin da wasu su ka sami munanan raunuka.”

Advertisement

Written by

Katsina City News

Katsina City News is a journalist and correspondent at Katsina Times — covering local, national and international news with a focus on Northern Nigeria.

Comments (0)

No comments yet. Be the first to share your thoughts!

Leave a Comment

What is 3 + 2?