Kwamitin Farfado da Martabar Wuraren Tarihi da Al’adun Jihar Katsina, wanda Maigirma Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim M. Ida, Ph.D., CON. ke jagoranta, ya bukaci jama’ar Jihar Katsina da su gabatar da shawarwari (memoranda) domin bayar da gudunmuwa wajen farfado da muhimman wuraren tarihi da bunkasa bukukuwan al’ada na hawan sallah a jihar.
Wannan yunkuri ya samu amincewar Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, Ph.D., CON., a wani bangare na kokarin gwamnati na kare tarihinta da habbaka al’adun gargajiya na masarautu.
A cewar wata sanarwa da Sakataren Kwamitin, Sani Rabiu Jibia, ya fitar a ranar 20 ga Yuni, 2025, an bukaci daukacin jama’a da masu ruwa da tsaki da su turo da shawarwarinsu a rubuce ta adireshin imel: ktsgheritage@gmail.com ko a kawo su kai tsaye zuwa: VIP No. 3, gab da Hukumar Ruwa ta Jihar Katsina (Water Board), GRA, Katsina.
Kwamitin ya bukaci hadin kan jama’a wajen samar da sabbin dabaru da hanyoyin da za su taimaka wajen inganta wuraren tarihi da al’adu, tare da tabbatar da ci gaban bukukuwan hawan sallah a jihar.
Kwamitin zai ci gaba da karbar shawarwari daga jama’a domin samun cikakkiyar fahimta da tasirin ra’ayoyin al’umma a cikin wannan muhimmin shiri na raya tarihi da al’adu a Jihar Katsina.