A duba lamarin Killace Wajen Hutawa na Kofar Soro


Nazari daga Katsina Times

Marigayi Galadiman Katsina, Mai Shari’a Mamman Nasir (Allah ya jikansa da rahama), shi ne ya jagoranci sake gina Kofar Soro, kamar yadda ya bayyana a wata hira da ya yi da Taskar Labarai a shekarar 2014, dangane da tarihin rayuwarsa.

A cikin hirar, Marigayi Mamman Nasir ya ce, sun tsara yadda za a gyara gaban kofar domin ya zama wajen hutuwa ga jama'a a kowane lokaci. Wannan mataki, a cewarsa, yana kara nuna martabar gidan Sarki da kuma karfafa alakar jama'a da masarauta. Sama da shekaru 50, gaban kofar Soro ya kasance wajen taruwa da hutu ga al'umma.

Sai dai a sabon gyaran da aka yi a shekarar 2024, an killace wajen da ake zama da waya, an kuma rufe shi da kwaɗo. Wannan mataki ya jawo cece-kuce daga jama’a, musamman a bayan fage, inda da dama ke ganin ba a yi nazari mai zurfi ba kafin daukar wannan mataki, kuma ba a tuntubi jama’a ba.

Wurin yana kan hanya mai yawan zirga-zirgar jama’a, wanda ke hade da asibiti, kasuwa, tashar mota ta Kofar Sauri, da makarantu. A yanzu ana ganin wajen za a rika bude shi sau biyu ne kacal a shekara — yayin Babbar Sallah da Karamar Sallah.

A sake duba wannan mataki, tare da nazarin amfanin bude wajen da kuma illar rufe shi, kafin yanke hukunci da ya fi dacewa da maslahar al’umma.

Follow Us