___Za'a Horar da Masu Sana’o’i 10,000 karkashin KATSINA TALENT HUNT CHALLENGE.
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, na shirin ci gaba da gina tubalin bunkasa baiwa da tsohon gwamna, Aminu Bello Masari, ya kafa, yayin da Cibiyar Talent Hunt da Innovation ta Jihar Katsina ke shirin horar da masu sana’o’i 10,000 daga ƙananan hukumomi 34 na jihar kan sana’o’in hannu da fasahohin zamani.
Shirin koyon sana’a da ƙarfafa tattalin arziki na tsawon watanni 18 zai fara ne a watan Satumba 2026, da nufin bai wa waɗanda za su amfana ƙwarewar da za su iya dogaro da ita, samun aikin yi da kuma ƙarfafa ƙwararrun ma’aikata a jihar.
Mai kula da Cibiyar, Faisal Jafar Rafindadi, ya bayyana hakan ne ranar Laraba a Abuja, yayin da yake bayani kan shirin cibiyar na sabon matakin bunƙasa baiwa da koyar da sana’o’i.
Rafindadi ya ce cibiyar ta kwashe kusan shekaru goma tana gano mutane masu baiwa iri-iri, tare da taimaka musu wajen haɓaka ƙwarewarsu da mayar da ita sana’ar dogaro da kai.
Ya ce horon zai ƙunshi sana’o’i da dama da suka haɗa da katako, aikin plaster, samarwa da shimfiɗa interlocking, aikin famfo, lantarki, POP, ƙera tagogi da ƙofofin aluminium, da kuma fasahar sadarwa (ICT).
Ya bayyana cewa za a horar da mutane 10,000 daga ƙananan hukumomi 34, inda za a samar musu da horo na zahiri da ƙwarewa a fannonin da suka zaɓa.
> “Manufar ita ce a ba mahalarta ƙwarewar da za ta taimaka musu su kafa sana’o’insu, samun aikin yi da kuma bayar da gudummawa wajen bunƙasa tattalin arzikin Jihar Katsina,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa za a aika da fom zuwa ƙananan hukumomi domin zaɓen waɗanda za su amfana, yayin da cibiyar da ke Katsina za ta jagoranci aiwatar da shirin baki ɗaya.
Haka kuma, cibiyar na shirin buɗe ofishinta a hukumance, wanda zai zama cibiyar gudanar da shirye-shiryen koyon sana’o’i, gano baiwa da bunƙasa ƙirƙire-ƙirƙire.
Ana sa ran Gwamna Radda zai ƙaddamar da cibiyar a wani mataki na ƙara ƙarfafa koyon sana’o’i da samar da damarmaki ga matasa da ƙwararrun ma’aikata.
Rafindadi ya ce cibiyar tana aiki tare da Katsina State Institute of Technology and Management da National Board for Technical Education (NBTE) domin tallafa wa shirin da faɗaɗa ayyukansa.
Ya bayyana kyakkyawan fata cewa shirin zai taimaka wajen bunƙasa kasuwanci, rage rashin aikin yi da bai wa matasa damar mayar da baiwarsu da ƙwarewar da suka samu zuwa hanyar samun abin dogaro na dindindin.
Shirin horar da masu sana’o’i 10,000 ya zama sabon babi a ci gaban Katsina National Talent Hunt Challenge, wanda aka ƙaddamar a ƙarshen shekarar 2020 a ƙarƙashin gwamnatin tsohon Gwamna Aminu Bello Masari.
An samar da shirin ne domin gano, haɓaka da kuma tallata ɓoyayyun baiwa da ƙwarewar matasan Jihar Katsina, tare da samar musu da hanyoyin samun abin yi da kuma nisantar ayyukan ta’addanci da sauran munanan ɗabi’u.
A farkon shirin, an samar da hanyoyin yin rajista da tantance masu baiwa daga sassa daban-daban na jihar domin su samu damar nuna ƙwarewarsu a fannoni daban-daban.
A watan Fabrairu 2022, an gudanar da ƙarshen gasar farko ta Katsina National Talent Hunt Challenge a Bello Kofar Bai Hall da ke Katsina, inda matasa suka fafata a fannoni da suka haɗa da ICT, fasaha da zane, ƙirar motoci, waƙa da nishaɗi, da sauran fannoni.


Comments (0)
No comments yet. Be the first to share your thoughts!